8 Satumba 2014 - 13:46
Magoya bayan UMP sun bukaci Sarkozy ya jagorance su

Taron shekara shekara na matasan jam’iyyar adawa ta kasar Faransa UMP ya bukaci tsohon shugaban kasar Nicolas Sarkozy da ya karbi ragamar jagoancin jam’iyyar domin tabbatar da samun nasararta a zabe na gaba.

Taron wanda aka gudanar a birnin Nice da ke gabashin kasar, ya samu halartar manyan jami’an jam’iyyar da suka hada da tsohon Firaminista Jean-Pierre Raffarin wadanda suka nuna alamun goyon baya ga Sarkozy.

Daya daga cikin manyan jami’an jam’iyyar kuma dan Majalisar Dokoki da ke wakiltar yankin na Nice Christian Estrosi, ya ce suna bukatar a dawo da tsohon shugaban kasar domin jagorantar jam’iyyar. ABNA